Koma ka ga abin da ke ciki

Koma ga abubuwan da ke ciki

WAƘA TA 109

Mu Kasance da Kauna ta Gaske

Mu Kasance da Kauna ta Gaske

(1 Bitrus 1:22)

  1. 1. Allah zai yi murna da mu

    In muna yin ƙauna sosai.

    Ƙauna na da muhimmanci,

    Halin Jehobah ne.

    In muna ƙauna da gaske

    Abokantaka zai yi kyau,

    Za mu mutunta mutane

    In muna da ƙauna.

    Zai dace mu taimaka

    In ’yan’uwa na da bukata,

    Domin hakan zai nuna

    Mun san yadda suke ji.

    Yesu ya nuna mana duk

    Irin ƙauna ta Allahnmu,

    Don mu riƙa nuna ƙauna,

    Ƙauna ga duk mutane.

    Mu zama masu ƙauna.

(Ka kuma duba 1 Bit. 2:17; 3:8; 4:8; 1 Yoh. 3:11.)