Koma ka ga abin da ke ciki

Koma ga abubuwan da ke ciki

WAƘA TA 4

“Jehobah Makiyayina Ne”

“Jehobah Makiyayina Ne”

(Zabura 23)

  1. 1. Jehobah ne Makiyayi,

    Ja-gorancinsa zan bi.

    Shi ne ya san duk tunanina,

    Ya san duk bukatuna.

    Ya kai ni wurin albarka,

    Inda akwai kyau sosai.

    Yana min ja-goranci da ƙauna

    Don in sami salama.

    Yana ja-goranci da ƙauna

    Don in sami salama.

  2. 2. Dokokinka na adalci

    Suna kwantar min da rai.

    Don sunanka ka taimaka min

    In riƙa yin nufinka.

    Ko ina cikin wahala,

    Ka kiyaye ni, Allah.

    Ba zan taɓa jin tsoron kome ba

    Domin kai ne Allahna.

    Ba za ni ji tsoron kome ba

    Domin kai ne Allahna.

  3. 3. Jehobah Makiyayina,

    Ja-gorancinka zan bi.

    Ka ƙarfafa ni, ka kāre ni,

    Ka biya bukatuna.

    Ina dogara gare ka,

    A dukan rayuwata.

    Bari ƙaunarka da kulawarka

    Su bi ni har abada.

    Bari ƙauna da kulawarka

    Su bi ni har abada.

(Ka kuma duba Zab. 28:9; 80:1.)