Koma ka ga abin da ke ciki

Koma ga abubuwan da ke ciki

WAƘA TA 53

Muna Shirin Fita Wa’azi

Muna Shirin Fita Wa’azi

(Irmiya 1:17)

  1. 1. Mun tashi

    Za mu fita

    Don mu je yin wa’azi.

    Ana yayyafi,

    Har da sanyi sosai.

    A lokacin ne fa yin barci

    ke daɗi.

    (AMSHI)

    Yin addu’a da kuma shiri

    Da fatan alheri,

    Za su ba mu ƙarfin zuciya

    Da muke so.

    Mala’iku da Yesu Kristi,

    Suna taimakon mu.

    Ga kuma dukan ʼyan’uwanmu,

    Sai godiya.

  2. 2. Za mu yi

    Murna sosai

    In mun bi umurnin nan.

    Allah na ganin

    Dukan ƙoƙarinmu.

    Yana tunawa da ƙaunarmu,

    ba shakka.

    (AMSHI)

    Yin addu’a da kuma shiri

    Da fatan alheri,

    Za su ba mu ƙarfin zuciya

    Da muke so.

    Mala’iku da Yesu Kristi,

    Suna taimakon mu.

    Ga kuma dukan ʼyan’uwanmu,

    Sai godiya.

(Ka kuma duba M. Wa. 11:4; Mat. 10:​5, 7; Luk. 10:1; Tit. 2:14.)